Leave a message

Breaking

Post Top Ad

| Latest News | Entertainment | Seince & Technology |Advertisement |Videos| Books | Love Quate & Others |

Thursday, 10 January 2019

TAMBAYA:Yanda Ake Gane Kabli Da Ba'adi Dakuma Yanda Ake Gyarasu.

TAMBAYATA 

Ask & Question.

Assalamu Alaikum tanbayata itace ya ake gane."kabli da ba'adi".Kuma ya ake gyara su.?

AMSA

Da farko mu sani cewar duk abinda yake farillane

a sallah kuma akabarshi to kabaliyyah ko ba’adiyyah

bata gyarashi, to haka hukuncin yake a salloli na nafila?.

Haka kuma duk abinda mustahabbine a sallah to shima

ba’a yi masa kabaliyyah ko ba’adiyyah.

Dukkan rafkannuwa da aka yi ta a lokacin da ake ramuwar

sallah to hukuncinta kamar sallar da ake yenta ne a cikin

lokaci, kenan ba banbanci da sallolin ramuwa da kuma

wadanda ake yinsu cikin lokaci.

Yin rafkannuwa a sallar nafila hukuncinsa kamar yin

ranfannuwa ne a sallolin farilla in banda mas’aloli guda

shida ananne nafila ta banbanta da farilla, sune kuma

kamar haka:

(1) Karatun Fatiha: Duk wanda ya manta da karatun fatiha

a sallar nafila bai tunaba sai bayan ya yi ruku’u sannan

ya tuna to anan zai ci gaba da sallar shine sai bayan ya

kammala ya yi kabaliyyah, sabanin sallar farilla da zai cire

wannan raka’ar ya kawo wata makwafinta sannan ya yi

ba’adiyyah idan ba’a biyun farko bane, ko kabaliyyah

idan hakan ya farune a biyun farko na farilla.

(2) Karatun Sura.

(3) Bayyanawa.

(4) Sirrantawa.

Idan mutum ya manta karatun sura bayan fatiha a cikin

sallar nafila, ko kuma ya bayyana a inda ake asurtawa ko

ya sirranta a inda ake bayyanawa kuma bai tunaba sai

bayan da ya yi ruku’i to zai ci gaba da sallar shine, amma

duka a cikin nafila to babu komai akansa, wato ba

kabaliyyah kuma ba ba’adiyyah, sabanin inda sallar

farilla ce.

(5) Tashi Zuwa Raka’a Ta Uku: Dun wanda ya kammala

raka’o’I biyu a sallar na fila sai bai zaunaba ya mike

zuwa raka’a ta uku to idan ya tuna kafin ya kulla ruku’u

to anan zai dawo ya zauna ya yi tahiya ya yi sallama,

sannan kuma ya yi ba’adiyyah, amma har idan ya kulla

raka’a ta uku to zai ci gabane da sallar sai ya karat a

zama raka’o’I hudu sannan sai ya yi kabaliyyah,

sabanin sallar farilla.

(6) Manta Rukuni: Duk wanda ya manta rukuni a sallar

nafila kamar ruku’i ko sujjada kuma bai tuna ba har ya yi

sallama kuma abin ma ya yi tsawo to anan ba zai sake

sallar ba, sabanin sallar farilla, domin inda farillace to da

zai sake sallarne har abada .

Kammalawa: Wadannan sune wuraren da aka dan sami

banbanci tsakanin salloli na farilla da salloli na nafila akan

abinda ya shafi hukunce-hukuncen rafkannuwa, da fatan

Allah yasa ya anfanar da mu.

Please Share and Comment

No comments:

Post a Comment

Comment

Post Top Ad

Your Ad Spot
+widget
a